Home / KUNGIYOYI / An Rantsar Da Sabbin Shugabannin NUJ Na Rediyon Aminci Kano

An Rantsar Da Sabbin Shugabannin NUJ Na Rediyon Aminci Kano

A kokarin ganin an tafiyar da ayyukan manema labarai kamar yadda ya dace kungiyar yan jarida reshen Gidan rediyon Aminci da ke Kano sun zabi sababbin shugabanni karkashin jagorancin Kwamared Aliyu Sufyan.

 

Kwamared Aliyu Sufyan wanda ya kasance edita ne kuma shugaban wani shirin siyasa da ake gabatarwa a gidan rediyon ya dauki rantsuwar yin shugabancin kungiyar NUJ reshen gidan rediyon tare da sauran jama a kamar haka.

Zabbabun shugabannin kenan a lokacin da suke Sanya hannu a rantsuwar kama aiki

Akwai mataimakin shugaba, Ummushakeer Ahmed, sakatare, Abubakar Haruna Galadanci, sakataren kudi,vSa’adatu Hussain Ya’u, Ma’ajin kungiyar, Shamsudden Mustapha Danhaki, Mai binciken kudi,  Garzali Jibril Maimashi Bebeji, sai kuma babban mai bincike, Shazali Farawa.

 

Ga dai hotunan taron rantsuwar nan kamar yadda zaku iya gani a cikin hotuna.

About andiya

Check Also

Zulum meets Tinubu over South Chad Irrigation Scheme

  .. Says Tinubu approves Gwoza FCE take off     Borno State Governor, Babagana …

Leave a Reply

Your email address will not be published.