Home / Lafiya / Gwamnan Jihar Kaduna Da Mataimakiyarsa Sun Karbi Allurar Rigakafin Korona

Gwamnan Jihar Kaduna Da Mataimakiyarsa Sun Karbi Allurar Rigakafin Korona

Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufa’i ya samu nasarar karbar allurarsa ta rigakafin cutar Korona da ke haddasa Mashako mai tsanani.
Gwamnan tare da mataimakiyarsa Dokta Hadiza Sabuwa Balarabe duk sun samu tasu allurar mai suna “Astra Zeneca” domin Rigakafin cutar Korona.
Ita dai cutar Korona ta addabi duniya baki daya wanda dalilin hakan tattalin arzikin duniya ya samu nakasa, saboda ayyuka,sana’o’i da kamfanoni da dama sun shiga cikin hali na tagayyara wasu ma da dama duk sun durkushe baki daya, hatta wadansu kasashe a yanzu na cikin mawuyacin halin kasa aiwatar da abin da ya dace su aiwatar.

About andiya

Check Also

Zulum meets Tinubu over South Chad Irrigation Scheme

  .. Says Tinubu approves Gwoza FCE take off     Borno State Governor, Babagana …

Leave a Reply

Your email address will not be published.