Home / Uncategorized / Masari Ya Kaddamar Da Motocin Kashe Gobara Guda Biyu

Masari Ya Kaddamar Da Motocin Kashe Gobara Guda Biyu

Masari Ya Kaddamar Da Motocin Kashe Gobara Guda Biyu

Mustapha Imrana Abdullahi

 

Gwamnan Jihar Katsina Rt. Hon. Aminu Bello Masari, ya kaddamar da Motocin Ƙashe gobara guda 2 ɗaya Shiyyar Daura, ɗaya kuma a makarantar kashe gobara ta Arewa masu Yamma da ke ƙaramar hukumar Kankiya wadda Sanator Ahmad Babba Kaita ya nemo a zauren majalisar Dattawa ta kasa.

An kaddamar da wadannan motoci ne a fadar Gwamnatin jihar katsina ƙarkashin Shugaban hukumar Kashe Gobara ta ƙasa Alhaji  Ibrahim Liman Alhaji, ya kawo wannan motoci domin damƙama Gwamnatin jihar katsina su kafin kai kowace mazauninta da za a ci gaba da aiki da su.

A cikin Jawabin Maigirma Gwamna Masari a lokacin da yake ƙaddamar da motocin ya yabama Sanator Ahmad Babba Kaita daya jajirce wajen kawo irin wannan ci gaba a jihar katsina, tare da hukumar kashe gobarar ta kasa da irin wannan kokari da suka yi domin ganin kafuwar wannan makaranta tare da zuwan wannan motoci jihar katsina.

 

About andiya

Check Also

Remain steadfast against security challenges” – CDS General Musa to army officers and men

  The Chief of Defence Staff , General Christopher Musa has tasked the Nigeria Army …

Leave a Reply

Your email address will not be published.