Home / Labarai / Muna Bukatar Yan Sandan  SARS  A Jihar Zamfara – Matawalle

Muna Bukatar Yan Sandan  SARS  A Jihar Zamfara – Matawalle

Muna Bukatar Yan Sandan  SARS  A Jihar Zamfara – Matawalle

Mustapha Imrana Andullahi
Gwamnan Jihar Zamfara Alhaji Dokta Muhammad Bello Matawallen Maradun ya bayyana cewa su a Jihar Zamfara suna bukatar jami’an tsaron yan sandan SARS saboda irin aikin da suke gudanarwa a Jihar.
Gwamna Matawalle ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai jim kadan bayan ya fito daga taron kungiyar Gwamnonin Arewacin Nijeriya da aka yi a Kaduna.
Matawalle ya ce su matsayinsu a Jihar Zamfara Shi ne suna bukatar jami’an tsaron yan Sandan SARS sakamakon irin kwazon aikinsu, don haka ya kara da cewa suna bukatar a zakulo su a duk inda suke a kawo masu su a Jihar Zamfara suna bukatarsu.

About andiya

Check Also

APC RELOCATES TO NEW STATE HEADQUARTERS IN GUSAU, ZAMFARA

The Zamfara State chapter of the All Progressives Congress APC has today relocated to its …

Leave a Reply

Your email address will not be published.