Home / Labarai / Sanata Hadi Sirika Ya Zagaya Tashoshin Jiragen Sama

Sanata Hadi Sirika Ya Zagaya Tashoshin Jiragen Sama

Mustapha  Abdullahi
A kokarin ganin an dawo da zirga zirgar tashi da sauka a tashoshin Jiragen kasar tarayyar Nijeriya ministan ma’aikatar kula da tashi da saukar Jiragen Sama Sanata Hadi Sirika ya zagaya tashoshin da aka bude domin ganin yadda lamarin ke gudana.
Kamar yadda ya bayyana a shafinsa na fezbuk ” Na zagaya tashoshin Abuja da Legas, ina kyautata zaton cewa mun samu nasarori kashi 95 cikin dari da za su sa mu sake bude tashoshin nan kamar yadda na zagaya su, tun bayan yaki da cutar Korona da tun farko tasa aka rufe tashoshin Jirage aka kuma hana sauka da tashin Jiragen baki daya,
saboda a halin yanzu kusan dukkan matakan kariya domin ci gaba da zirga zirgar fasinjoji da Jirage duk an tanaje su baki daya”, inji Minista Hadi Sirika, na Buhari.

About andiya

Check Also

Zulum meets Tinubu over South Chad Irrigation Scheme

  .. Says Tinubu approves Gwoza FCE take off     Borno State Governor, Babagana …

Leave a Reply

Your email address will not be published.