Home / Big News / Yan Sanda Sun Kama Motar Kifi Dauke Da Mutane 91 A Kaduna

Yan Sanda Sun Kama Motar Kifi Dauke Da Mutane 91 A Kaduna

Kwamishinan Yan sandan Jihar Kaduna Umar Musa Muri, ya bayyana wa manema labarai cewa sun kama wata motar daukar Kifi dauke da Mutane 91, Awaki da Babura a babban titin garin kaduna na Yamma da ake cewa bypass.
Kwamishinan ya bayyana cewa sun kama direban motar mai suna Abdurrazak da ya shaida masu cewa motar ta taso ne daga Jihar Katsina kuma mallakar wani kamfanin kifi ne a Katsina kuma zai kai mutanen ne garin Legas.
Kamar yadda direban ya shaidawa manema labarai bayan da Jami’an yan sanda suka yi nasarar kama shi da motar ya ce daga Katsina ya taso kuma ya dauko mutanen ne a garin Zariya kuma zai kai su Legas, sai dai ya tabbatar da cewa ba shi ne ya yi wa motar Lodin ba.
Indai za a iya tunawa irin wannan tafiya zuwa garin Legas da za a hada tarin mutane da Dabbobi da kuma Baburan hawa daga arewacin Nijeriya ba sabon abu bane kasancewar wasu yan Arewa da yawa sun saba da hakan tsawon lokaci.
Saboda a wasu lokuta zaka ga mutanen da ke son zuwa Legas neman kudi ko garin Lokwaja sun Saba da hawan manyan motoci domin kawai neman sauki.

About andiya

Check Also

Agriculture: Mrs Tinubu empowers 140 North west women farmers as Gov Idris enhances sustained farmers , women capacity for nation building

By Suleiman Adamu, Sokoto At least , 140 Northwest women farmers in Kebbi state benefitted …

Leave a Reply

Your email address will not be published.