Home / Ilimi / Za’A Gina Dakin Rainon Yara A Makarantar Kawo

Za’A Gina Dakin Rainon Yara A Makarantar Kawo

Daga Dan Kaduna Abdullahi
Kwamishinan kula da ma’aikatar ilimin Jihar Kaduna Dakta Shehu Muhammad ya bayyana cewa za a gina ingantaccen dakin rainon yara a makarantar sakandare ta Kawo cikin garin kaduna.
Kwamishina shehu Muhammad ya bayyana hakan ne a lokacin da shi da tawagarsa suka kai ziyarar gani da ido yadda harkokin koyarwa da kuma yadda yara dalibai suka dawo makaranta tun bayan dawowa daga hutu a jihar.
Kwamishinan ya ci gaba da babban dalilin da yasa za a gina wannan dakin rainon yara shi ne saboda irin yadda mata malamai suke da yawa da suka kai shittin (60) a wannan makaranta, saboda idan an gina wannan dakin raino zai ba malaman mata damar su gudanar da aikinsu na koyar da dalibai kamar yadda ya dace.
Ya kuma ce za a gina karin Ajujuwa da Ban dakuna domin zagaya wa ga duk masu bukatar yin haka  a makarantar.
Duk da kamar yadda Kwamishinan ilimin ya bayyana cewa dalibai sun dawo a kan Kari, ya kuma yi kira ga iyayen yara da su kokarta domin ganin yayansu sun dawo makarantar saboda lokacin karatu ba zai jira kowa ba.
Ko a cikin wata sanarwar da ma aikatar ilimin Jihar karkashin jagorancin Dakta Shehu Muhammad ta bayyana cewa za a hukunta masu kunnen kashin da suka kasa dawowa makaranta a kan kari.

About andiya

Check Also

Sokoto state government dethrones 15 traditional leaders, four others being investigated for various offences

  By S. Adamu, Sokoto Fifteen Sokoto traditional leaders have been dethroned by the Sokoto …

Leave a Reply

Your email address will not be published.