Home / Uncategorized / An Ga Watan Azumin Ramadana – Mai Alfarma Sarkin Misilmi

An Ga Watan Azumin Ramadana – Mai Alfarma Sarkin Misilmi

Fadar mai alfarma sarkin Musulmin Najeriya, Alhaji Dokta Sa’ad Abubakar ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan da maraicen ranar Juma’a.
Cikin wata sanarwa da Sarkin Musulmin, Sa’ad Abubakar lll ya karanta a fadarsa, ya ce an ga watan a sassan ƙasar daban-daban.
Don haka ne ya ayyana ranar Asabar 1 ga watan Maris a matsayin 1 ga watan Ramadan 1446.
Tuni dai hukumomin Saudiyya suka sanar da ganin watan a ƙasar, inda suka ayyana gobe Asabar a matsayin ɗaya ga watan Ramadan a Saudiyya.

About andiya

Check Also

Federal Government Partners with UNDP to Train and Certify Technicians in the Refrigeration and Air-Conditioning Sector

By; Imrana Abdullahi Abuja, Nigeria – 21 August 2025 – The Federal Government of Nigeria, …

Leave a Reply

Your email address will not be published.