Home / Uncategorized / An Ga Watan Azumin Ramadana – Mai Alfarma Sarkin Misilmi

An Ga Watan Azumin Ramadana – Mai Alfarma Sarkin Misilmi

Fadar mai alfarma sarkin Musulmin Najeriya, Alhaji Dokta Sa’ad Abubakar ta sanar da ganin jinjirin watan Ramadan da maraicen ranar Juma’a.
Cikin wata sanarwa da Sarkin Musulmin, Sa’ad Abubakar lll ya karanta a fadarsa, ya ce an ga watan a sassan ƙasar daban-daban.
Don haka ne ya ayyana ranar Asabar 1 ga watan Maris a matsayin 1 ga watan Ramadan 1446.
Tuni dai hukumomin Saudiyya suka sanar da ganin watan a ƙasar, inda suka ayyana gobe Asabar a matsayin ɗaya ga watan Ramadan a Saudiyya.

About andiya

Check Also

21 Kogi LGA Chairmen, 239 Councillors Endorse Governor Ododo for Second Term

    Chairmen of the 21 Local Government Areas alongside the Forum of Councillors of …

Leave a Reply

Your email address will not be published.