Daga Mai Girma, Jakada Dr. Malami Shehu Ma’aji (MFR) Shugaban, Kwamitin Shawara, Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta Duniya (Nigeria)
Mai Ba da Shawara na Musamman ga Huldar Kasa da Kasa a Nahiyar Afrika
Da sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai.
Yayin da wannan wata mai albarka na Ramadan ya iso, ina mika gaisuwa ta musamman ga dukkan Musulmi a fadin Najeriya, Afrika, da duniya baki daya.
Ramadan wata ne mai tsarki na tunani, tausayi, hakuri, da sabunta ibada ga Allah (SWT). Wata ne da ke tunatar da mu kan ɗan adam ɗaya da kuma nauyin da muka dauka na tallafa wa juna.
Wannan wata mai tsarki yana kira gare mu da mu karfafa dabi’un zaman lafiya, hakuri, adalci, da rahama.
Bayan azumin abinci da abin sha, Ramadan yana koya mana tsarkake zukatanmu, gyara halayenmu, da kuma sabunta niyyarmu wajen aikata alheri, karamci, da hidima ga al’umma.
A wannan lokaci da al’ummominmu da kasashenmu ke fuskantar kalubalen zamantakewa, tattalin arziki, da jin kai, Ramadan yana ba mu damar musamman ta gina hadin kai, juriya, da fahimtar juna. Mu yi amfani da wannan lokaci wajen kawar da bambance-bambance, tallafa wa marasa karfi, da kuma inganta zaman lafiya a cikin iyalanmu, makwabta da sauran alumma.
Ina kira ga dukkan ‘yan kasa da su rungumi hakikanin ruhin Ramadan ta hanyar nuna tausayi ga marasa galihu, girmama mutuncin juna, da kuma bayar da gudummawa mai kyau ga ci gaban kasa. Tare da aikata gaskiya a cikin imani da kuma alheri na hadin kai, za mu iya gina al’umma mai adalci, zaman lafiya, da tausayi.
Allah (SWT) ya karɓi azuminmu, addu’o’inmu, da rokonmu da sauran ibadun mu Amin. Allah ya gafarta mana, ya shiryar da mu, ya kuma albarkace mu da ni’ima mai yawa. Allah ya sa wannan Ramadan ya kawo zaman lafiya a gidajenmu, ci gaba ga kasarmu, da fata mai kyau ga ɗan adam.
Ramadan Mubarak.
Jakada Dr. Malami Shehu Ma’aji (MFR)
Shugaban, Kwamitin Shawara
Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta Duniya (Nigeria)
Mai Ba da Shawara na Musamman ga Huldar Kasa da Kasa a Nahiyar Afrika
THESHIELD Garkuwa