Home / Labarai / Masari, Ganduje sun kawo ziyara ta’azziya ga Gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.

Masari, Ganduje sun kawo ziyara ta’azziya ga Gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.

 

Gwamnonin jihohin Katsina, Aminu Bello Masari da na Kano Abdullahi Ganduje sun ziyarce Gwamnan jahar Sokoto da maraicen yau a Sokoto don gabatar da sakonni gwamnati da al’ummar jihohin su dangane da kisan gilla da aka yiwa wasu matafiya a garin Sabon Birni da sauran haren haren ta’addanci da suka faru a lokuta dabam dabam a jihar Sokoto.

 

Gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ne ya karbi bakuncin su tare da sauran mukkaraban gwamnatin jaha.

 

 

Allah Ya saka da alheri ya kawo saukin wadanan matsalolin, ameen.

Dingyadi Media

About andiya

Check Also

Q1: More Nigerians buy Dangote Cement, as volume rises by 26.1% to 4.6MT 

  Strategies adopted by Dangote Cement to increase sales and ensure an adequate supply of …

Leave a Reply

Your email address will not be published.