“Sule Lamido mutum ne mai muhimmanci a sabon tsarin gina Najeriya,” in ji Fasto Nnamdi Orji na God’s Glorious Time Redemption Ministry da ke Abuja.
Fasto Orji ya bayyana wannan a makon nan yayin tattaunawa da wasu mambobin coci kan abin da Allah ya nuna masa a matsayin wani bangare na abubuwan da za su haifar da sabuwar rayuwar ƙasa.
Ya ce Allah ya nuna masa yadda tsohon Minista kuma Gwamna zai taka muhimmiyar rawa a babban aikin taimaka wa kasa.
A halin yanzu, tsohon Gwamna Sule Lamido yana kallon yadda abubuwa ke gudana a ƙasar, musamman yadda jam’iyyun siyasa ke shirin zabukan 2027. Shiru da yake yi bai rage darajar siyasar sa ba a fadin ƙasa. Fasto Orji ya bayyana cewa Sule Lamido yana da manufa ta Allah wadda masu sharhi na siyasa ba su fahimta ba tukuna.
“Ina iya cewa ba zan iya tabbatar maka ba ko wannan manufa tana faruwa yanzu, ko a cikin watanni masu zuwa, ko a 2027, ko a nan gaba. Amma abu guda da zan tabbatar maka da shi shi ne, shi kaɗai ne ɗan Najeriya da Allah ya naɗa kuma ya shirya I don wannan manufa. Lallai ‘yan Najeriya za su gane tasirinsa a watanni masu zuwa.”
Binciken da masu sharhi na siyasa suka yi ya nuna cewa tsohon gwamna Lamido jagora ne mai son kowa da tsantsar aiki a hidimar jama’a.
Shi mai fafutukar fahimtar addini da juriya ne a ƙasar da wasu fitattun mutane ke amfani da addini wajen cimma manufofin siyasa ko na mugunta.
Ya yi aiki a matsayin Ministan Harkokin Waje a zamanin tsohon shugaban Olusegun Obasanjo daga 1999-2003, sannan ya zama gwamna na jihar Jigawa sau biyu daga 2007-2015. A lokacin gwamnatinsa ya kawo ci gaba mai sauyi a Jigawa, musamman a fannin ilimin musamman da kuma gine-gine.
A yau, jihar ba ta yawan shiga labarai saboda mummunan dalilai, sabanin yadda ake gani a wasu jihohin Arewa.
Fasto Orji ya kara da cewa: “Girman kai bai kamata ya hana ‘yan Najeriya daga kowane bangare neman hikimar siyasa da jagoranci daga wannan mutum ba. Sule Lamido Allah ya naɗa shi don ya jagoranci. Mu kula mu saurari muryar Allah Madaukaki, domin babu wanda ya san yadda da lokacin da manufarSa za ta tabbata, amma tabbas za ta tabbata.”
Faston ya kammala da cewa: “Allah ya nuna min Sule Lamido a matsayin cibiyar taron farin ciki na mutane da dama, duk suna sauraron sa kuma suna bin sa da yardar rai zuwa gari mai kyau da zaman lafiya. Bari shi kansa ya nemi fuskar Allah a kan waɗannan abubuwa, Dominic hanyoyin Allah ba su daidai da hanyoyin mutum.”
Faston ya yi amfani da wannan dama wajen kira ga ‘yan Najeriya su kasance masu addu’a da tsayin daka wajen neman fuskar Allah a dukkan lamura. Ya yi kira
musamman ga ‘yan Najeriya su rika yi wa shugabanninsu addu’a domin su ci gaba da yin manufofi da tsoron Allah.
Abuja based Pastor Nnamdi Orji of God’s Glorious Time Redemption Ministry. Tel. 08037095513. Email address orjinnamdi90@gmail.com
THESHIELD Garkuwa