Home / Labarai / An Kara Dokar Hana Fita A Kaduna Da Sati Biyu

An Kara Dokar Hana Fita A Kaduna Da Sati Biyu

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna Dakta Hadiza Balarabe, ta bayyana wa al’ummar Jihar cewa ta kara Sanya dokar hana fita da sati biyu.
A cikin sanarwar da ta fitar ta yi godiya ga al’ummar Jihar Kaduna bisa irin yadda suka yi biyayya a kwanaki 60 wato tsawon watanni 2 da aka rika Sanya dokar na kwanaki 30 day biyu.
Kuma sanarwar ta bayyana cewa za a rika fita a halin yanzu na kwanaki uku wato ranakun Talata, Laraba da Alhamis, wato an samu karin kwana daya kenan sabanin da da ake yin kwanaki 2 a sati.
Idan aka duba dai za a ga a cikin sati biyun za a yi kwanaki Takwas kenan cikin Dokar hana fita sauran ranakun kuma za a rika samun walwala.
Wannan sanarwar dai ta biyo bayan karewar kwanaki 30 da Gwamnatin Jihar ta bayyana na dokar a baya.
Sanarwar kuma ta ci gaba da fadakar da jama’a bukatar da ke akwai na yin biyayya ga dokar dakile cutar Covid – 19 da ake kira da Korona bairus.
Da suka hada da a rika wanke hannu, yin amfani da Takunkumin rufe baki da hanci da kuma bayar da tazara tsakanin jama’a tare da kiyaye duk wani taron jama’a.

About andiya

Check Also

AGILE project trains 2,400 on schools improvement plans in Sokoto 

By; S. Adamu, Sokoto A socio-education project driven organisation , the Adolescence Girls Initiative for …

Leave a Reply

Your email address will not be published.