Home / Labarai / Dankishin Kasa Ya Daura Tutar Najeriya A Kan Gidansa

Dankishin Kasa Ya Daura Tutar Najeriya A Kan Gidansa

Mustapha Imrana Abdullahi
Wani dan kishin kasa da ke zaune a cikin garin Kaduna arewacin tarayyar Najeriya ya bukaci al’ummar kasar da su rika Sanya batun kishin kansu da kasarsu a gaba a koda yaushe domin komai ya kara inganta.

Mai kishin kasar ya ce saboda irin kishin da yake yi wa kasarsa ta haihuwa  ya sa ya Daura tutar Najeriya a kan gidansa da nufin kowa ya ga misalin yadda ake bayyana kishin kasa a wasu kasashen duniya da suka ci gaba.
“Na halarci wadansu kasashe a duniya kuma na ga irin yadda jama’ar kasar ke nuna kishin kasa ta hanyar Daura tutar kasar a kan gidajensu wanda hakan na nuni da kishin kasarsu a fili, saboda haka ne muke kokarin nunawa jama’a domin kowa ya dauki sahun yin hakan”, inji dan kishin kasan.
Za a dai iya ganin hoton gidan da ke dauke da tutar Najeriya kamar yadda yake a hoton gidan.

About andiya

Check Also

Zulum meets Tinubu over South Chad Irrigation Scheme

  .. Says Tinubu approves Gwoza FCE take off     Borno State Governor, Babagana …

Leave a Reply

Your email address will not be published.