Home / Labarai / Gwamna Matawalle Ya Nada Sabon Sarkin Kauran Namoda

Gwamna Matawalle Ya Nada Sabon Sarkin Kauran Namoda

Imrana Abdullahi
Gwamnan Jihar Zamfara Bello Mohammed ( Matawallen Maradun) MON, ya tabbatar da nadin Alhaji Sanusi Mohammed a matsayin sabon Sarkin Kauran Namoda.
 Amincewa ta biyo bayan irin shawarar da majalisar zaben Sarki a masarautar Kauran Namoda ta bayar ne kamar yadda yake kunshe a cikin kundin tsarin dokokin masarautar.
Alhaji Sanusi Mohammed ya Gaji tsohon Sarkin ne Alhaji Mohammed Ahmed Asha wanda ya rasu bayan gajeruwar rashin lafiya.
Ga hoton sabon sarkin kauaran Namoda a Jihar Zamfara yana cikin kakin soja
Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takardar da ke dauke da sa hannun Zailani Bappa, mai ba Gwamnan Zamfara shawara a kan harkokin wayar da kan jama’a da kuma kafafen yada labarai.
Kafin nadin nasa dan shekaru 40 Alhaji Sanusi Mohammed yana aiki da rundunar sojan Nijeriya ne a matsayin Mejo.
 Yayin da Gwamnan yake yin addu’ar Allah jikan mamacin wato tsohon sarki, Gwamna Matawalle ya kuma yi wa sabon Sarkin matan samun nasara a lokacin Mulkinsa.

About andiya

Check Also

WE MUST DEPLOY ADVANCED TECHNOLOGY TO FIGHT INSECURITY, GOVERNOR LAWAL TELLS UNITED NATIONS 

By; Imrana Abdullahi, Kaduna Governor Dauda Lawal has emphasized the pressing need to deploy advanced …

Leave a Reply

Your email address will not be published.