Home / News / Hukumar Zaben Kaduna Ta Dage Zaben Kananan Hukumomi Hudu

Hukumar Zaben Kaduna Ta Dage Zaben Kananan Hukumomi Hudu

Mustapha Imrana Abdullahi

Hukumar zabe mai zaman kanta a Jihar Kaduna (KADSIECOM) ta sanar da dage zaben kananan hukumomi guda hudu a Jihar.

Shugabar hukumar Dokta Saratu Binta Dikko – Audu, ta bayyana hakan a wajen wani taron manema labarai a ofishin hukumar da ke Kaduna, a ranar Juma’a 3 ga watan Satumba 2021.

“An tabbatar mana da cewa a cikin Jihar nan da akwai rahoton batun matsalar tsaro don haka ba za a samu damar yin zabe a wasu kananan hukumomi ba”, inji Saratu Dikko Audu.

Saboda haka domin a kare rayuwa da dukiyoyin mutane da suka hada da masu zabe da kayan zaben don haka dole sai mun Dakatar da zaben a wasu kananan hukumomi sai nan gaba za a sanar da ranar da za a yi zabe a nan gaba

“Don haka hukumar zabe mai zaman kanta ke sanar da Dakatar da yin zabe a wadannan kananan hukumomin da suka hada da 1- Birnin Gwari 2- Chikun 3- Kajuru 4 – Zangon Kataf”, inji Saratu.

Za a tabbatar da an kai wadatattun jami’an tsaro a wadannan kananan hukumomi domin kare lafiya da dukiyar jama’a “, inji ta.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Jihar Kaduna ta kuma sanar da ranar 25 ga watan Satumba 2021 a matsayin ranar da za a yi zabe a wadannan kananan hukumomi hudu da aka sage zabensu.

 

About andiya

Check Also

Group Decries Escalation Of  Insecurity In Birnin Gwari

      By; Our Reporter in Kaduna   The Birnin Gwari Progressive Union(BEPU) has …

Leave a Reply

Your email address will not be published.