Home / Lafiya / Na Gano Maganin Korona Bairus – Forofesa Ayodele 

Na Gano Maganin Korona Bairus – Forofesa Ayodele 

Furofesa Ayodele Israel Adeleye daga Jihar Kaduna a tarayyar Nijeriya ya bayyana cewa ya gano maganin kwayar cutar Covid – 19 da ake kira Korona da ta addabi duniya a halin yanzu.
Furodesa Ayodele ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a kaduna inda ya sha alwashin cewa yana son Gwamnati ta bashi mutane biyar da zai yi wa maganin cutar Korona birus kyauta domin a tantance gaskiyar maganinsa.
Ya kuma shaidawa manema labarai cewa maganin da ya gano zai magance suk wata matsalar da ake fama da ita a kan wannan kwayar cuta ciki har da batun rufe jama’a cikin gidaje sakamakon hana su fita.
 Furofesa Ayodele Israel Adeleye wanda ya kasance a kan gaba wajen bincike da a kan kimiyyar fasahar Gwaje gwaje ya tabbatarwa da manema labarai cewa a shirye yake ya warkar da mutane biyar da ke da cutar Korona Bairus kyauta domin ya fayyace gaskiyar maganinsa da yake bayani a kansa saboda yan Nijeriya da duniya baki daya.
Furofesa Adeleye wanda ya kasance tsohon Malami ne a jami’ar Ahmadu Bello kuma tsohon ma’aikaci a Asibitin koyarwa na jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, yana kira ga daukacin jami’an Gwamnati a dukkan mataki da kuma masu ruwa da tsaki a kan harkar lafiya da kada su yi kasa a Gwiwa wajen jaraba wannan maganin nasa domin amfanin al’umma, kasancewar cutar Covid – 19 da ake kira da Korona bairus na yin Illa ga ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

About andiya

Check Also

Zulum meets Tinubu over South Chad Irrigation Scheme

  .. Says Tinubu approves Gwoza FCE take off     Borno State Governor, Babagana …

Leave a Reply

Your email address will not be published.