Home / Labarai / SHUGABAN KASA TINUBU ZAI YI WA AL’UMMAR KASA JAWABI DA KARFE 7 NA YAMMA

SHUGABAN KASA TINUBU ZAI YI WA AL’UMMAR KASA JAWABI DA KARFE 7 NA YAMMA

Daga Imrana Abdullahi

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabi ga al’ummar kasar a ranar Litinin, 31 ga Yuli, 2023 da karfe 7 na yamma.

Bayanin hakan na kunshe ne  cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Dele Alake
Mai bawa shugaban kasa shawara na musamman (Ayyuka na musamman, Sadarwa & Dabaru) da aka fitar domin sanar da jama’ar kasa.

An umurci gidajen Talabijin da gidajen rediyo da sauran kafafen yada labarai na zamani da su rika cudanya da ayyukan sadarwar Hukumar Talabijin ta Najeriya da Rediyon Najeriya domin yada shirye-shiryen jawabin da shugaban kasar zai yi da Yammacin yau.

About andiya

Check Also

KASUPDA Organizes Stakeholders Engagement Programme

Community in the approved regularization layouts areas in Kaduna Metropolis have been advised to co- …

Leave a Reply

Your email address will not be published.