Home / News / AN SOKE TARON SHUGABANNIN ZARTASWAN APC NA KASA A RANAR ALHAMIS

AN SOKE TARON SHUGABANNIN ZARTASWAN APC NA KASA A RANAR ALHAMIS

MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI
Kamar yadda wata sanarwar da ta fito mai dauke da sa hannun sakataren babban kwamitin rikon jam’iyyar APC kuma sakataren kwamitin shirya zaben shugabannin na kasa Sanata Dokta John James Akpanudoedehe, ya sanyawa hannu da mai magana da yawun jam’iyyar APC Alhaji Salisu Na’inna Dan batta, ya aiko mana da sanarwar
Takardar ta ci gaba da bayanin cewa kamar yadda aka umarce ni daga shugaban kwamitin rikon jam’iyyar APC na kasa kuma shugaban babban kwamitin shirya zaben shigabanni na kasa Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni, cewa in sanar da soke taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da aka shirya yi a matakin kasa a ranar Alhamis 17 ga watan Maris 2022 don haka an soke wannan taro.

About andiya

Check Also

PDP Youth Leader Commends Hon Umar Yabo

The People’s Democratic Party ( PDP) Northwest Zonal Youth leader Alhaji Atiku Muhammad Yabo, the …

Leave a Reply

Your email address will not be published.