Home / Labarai / AYI HAKURI A ZABI JAM’IYYAR APC – BUHARI

AYI HAKURI A ZABI JAM’IYYAR APC – BUHARI

 

DAGA IMRANA ABDULLAHI
Shugaban kasar tarayyar Najeriya M7hammadu Buhari ya bayar da hakuri ga daukacin al’ummar Jihar Katsina da su yi hakuri su zabi jam’iyyar APC a zaben Gwamnoni da na yan majalisar Jiha mai zuwa
Muhammadu Buhari ya bayyana dan takarar Gwamnan Jihar Katsina Dokta Dikko Umar Radda a matsayin kwararren mutum mai dimbin basira dabzai yi amfani da kwarewarsa wajen ciyar da Jihar Katsina gaba.
Muhammadu Buhari ya bayyana hakan ne a cikin wani sakon faifan bidiyon da ya aikewa jama’a inda yake bayar da hakuri ga jama’ar cewa batun lamarin sake Fasalin  kudi da aka yi a halin yanzu ba an yi bane da gangan.
Jama’ a dai na ta tofa albarkacin bakinsu game da wannan bidiyon na shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yazo ne tun bayan da jama’ar Jihar suka bayyana matsayinsu a zaben shugaban kasa da yan majalisun Dattawa da na tarayya, shi yasa ake ganin Buhari tare da wadanda suka san dadin Gwamnati a matakan Jiha da na kasa suke ganin ya dace aba jama’a hakuri su ci gaba da zaben APC da Buhari yake ciki.

About andiya

Check Also

Dangote crashes Diesel price to N1,000 per litre

In an unprecedented move, Dangote Petroleum Refinery has announced a further reduction of the price of diesel from …

Leave a Reply

Your email address will not be published.