Home / Labarai / BUHARI YA KARA WA’ADIN CANZA KUDI DA KWANAKI GOMA (10)

BUHARI YA KARA WA’ADIN CANZA KUDI DA KWANAKI GOMA (10)

…RANAR 10 GA WATAN FABRAIRU

GWAMNAN  babban Bank8n Najetiya, Godwin Emefiele, ya sanar da cewa an yi karin kwanaki Goma domin a samu kammala hada hadar canjin sababbin takardun kudi da Kwanaki Goma.

Kamar yadda Gwamnan Bankin ya sanar a cikin wata takardar da aka rabawa manema labarai a ranar Lahadi, ya tabbatar da cewa an kara lokacin da kwana Goma

Gwamnan Bankin ya ce sun samu umarni ne daga shugaban kasa na karin kwanaki Goma domin yin canjin sababbin takardun kudin.

“Hakika mun nemi karin lokaci daga wurin shugaban kasa na kwanaki Goma daga ranar 31 ga watan Janairu, 2023 zuwa 10 ga watan Fabrairu 2023 domin jama’a su samu damar kammala samun takardun kudin da Doka ta amince da ayi amfani da su”.

About andiya

Check Also

Northern Christian Leaders Pay Homage to Khalifah Sanusi, Strengthening Ties.

Northern Nigerian Christian Clerics Pay Homage to His Highness Khalifah Sanusi Lamido Sanusi to Strengthen …

Leave a Reply

Your email address will not be published.