Home / Labarai / Gwamna Dikko Radda Zai Dauki Nauyin Hazikin Dalibi Mai Zanen Motoci

Gwamna Dikko Radda Zai Dauki Nauyin Hazikin Dalibi Mai Zanen Motoci

Daga Imrana Abdullahi
A kokarin da Gwamna Dokta Dikko Umar Radda na ganin an samu ingantacciyar hanyar samu hazikan masana da ke kawo ci gaba ya hanyar ilimi yasa  Gwamnatin jihar Katsina ta kudiri aniyar daukar nauyin karatun hazikin dalibin da ya ke zanen motoci don karatu a kasar Ingila
Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun Isah Miqdad, babban mai bayar da shawara ga Gwamna Dikko Radda a kan harkokin kafafen yada labarai na zamani
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,a ranar Alhamis, ya sha alwashin daukar nauyin karatun dalibin nan mai shekaru 17 Al’amin Sabitu, da yake da hazakar zane-zanen motoci domin ya yi karatun zanen motoci a kasar Ingila.
Da yake magana a lokacin da ya karbi bakuncin Al’amin Sabitu a ofishinsa, Malam Dikko Umaru Radda PhD ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da bada gudunmuwa ga duk dalibin da ya yi fice a fagen da ya sa gaba, somin su cigaba da karatu don cimma burinsu.
Gwamna Malam Dikko Radda ya umurci hukumar kula da ba da tallafin karatu ta ‘Scholarship Board’ da ta fara aikin yadda za ta samar wa yaron takardar ‘admission’ a jami’ar Coventry domin ya nazarci zane-zanen motoci a kasar ta Ingila.
Al’amin Sabitu dai ya fito ne daga mazabar Jiba na karamar hukumar Danja ta jihar Katsina, ya kammala karatun sakandare ne a kwanan nan a makarantar Demonstration da ke Zaria, jihar Kaduna.
Fata dai Allah ya kara daukaka Jihar Katsina da al’ummarta tare da kasa baki daya a kan harkokin ci gaba ta ko’ina.

About andiya

Check Also

Q1: More Nigerians buy Dangote Cement, as volume rises by 26.1% to 4.6MT 

  Strategies adopted by Dangote Cement to increase sales and ensure an adequate supply of …

Leave a Reply

Your email address will not be published.