Home / Labarai / GWAMNAN JIGAWA YA NADA JAMI’AN YADA LABARAI

GWAMNAN JIGAWA YA NADA JAMI’AN YADA LABARAI

Daga Imrana Abdullahi

A kokarin ganin an fadakar da daukacin dukkan jama’a game da irin abubuwan da ke faruwa na Gwamnati a Jihar Jigawa yasa Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya amince da nadin Hamisu Gumel a matsayin babban sakataren yada labaran sa.

Bayanin h akan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar, SSG, Bala Ibrahim, da aka  rabawa manema labarai ranar Talata a garin  Dutse hedikwatar Jihar.

Takardar sanarwar ta kara da cewa an nada Muhammad Salisu mataimaki na musamman ga gwamna kan harkar daukar hoto da yada labarai.

Sauran sun hada da Garba Hadejia da Umar Suleiman a matsayin mataimaka na musamman, sabbin kafafen yada labarai na yanar Gizo da biliyoyin al’umma ke amfani da su Dare da rana safe da Yamma.

About andiya

Check Also

APC National Chairman, Ganduje Commissions Road Named After Him in Gombe

  …Lauds Governor Inuwa’s Examplary Leadership …Says “President Tinubu, APC Leadership Proud of Gombe Governor’s …

Leave a Reply

Your email address will not be published.