Home / Labarai / Gwamnan Neja Ya Amince Da Rusa Hukumomi, Ma’aikatun Gwamnati A Jihar

Gwamnan Neja Ya Amince Da Rusa Hukumomi, Ma’aikatun Gwamnati A Jihar

Daga Imrana Abdullahi

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago ya amince da Rusa wasu hukumomi da Ma’aikatun Gwamnatin Jihar.

Sanarwar da Sakataren Gwamnatin Jihar  Abubakar Usman ya fitar a ranar Litinin, ta kuma sanar da soke duk wasu nade-naden siyasa da aka yi kafin ranar 29 ga Mayu, 2023.

A cewar sanarwar, rushewar  ta hada da na ka’ida da na hukumar da ba na doka ba

A yayin da Sakataren Gwamnatin ya yaba  da irin gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar da kuma harkokin ofishinsu.

Sanarwar ta kuma umarci hukumomin da abin ya shafa da su mika dukkan kadarorin gwamnati da suka hada da motocin hukuma da ke hannunsu ga babban Daraktan da ke hukumar da suke aiki .

About andiya

Check Also

MAY DAY 2024: GOV. DAUDA LAWAL RENEWS COMMITMENT TO IMPROVE WELFARE OF ZAMFARA WORKERS

By; Imrana Abdullahi Governor Dauda Lawal reiterated his administration’s commitment to improving the well-being of …

Leave a Reply

Your email address will not be published.