Daga Imrana Abdullahi
Babbar Kotun Gwamnatin tarayya da ke zamanta a Unguwar NDA cikin garin Kaduna ta bayar da Belin tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufa’i
Kamar dai yadda kotun ta ce ta bayar da Belin sa ne bisa wadansu sharudda.
Babban dan tsohon Gwamnan wanda ya kasance dan majalisar tarayya a halin yanzu mai wakiltar karamar hukumar Kaduna ta Arewa Honarabul Bello Nasiru El-Rufa’i ya shaidawa manema labarai irin farin ciki da jin dadin da suke da shi a wannan rana inda yake ta yi wa Allah hamdala da godiya bisa wannan Belin.

Inda ya ce za su tabbatar an cika sharuddan Belin da aka gindaya masa domin Belin.
THESHIELD Garkuwa