Home / Labarai / Da dumi duminsa: Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Wanke Dauda Lawal Dare A Matsayin Dantakarar Gwamnan Zamfara

Da dumi duminsa: Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Wanke Dauda Lawal Dare A Matsayin Dantakarar Gwamnan Zamfara

 

IMRANA ABDULLAHI (NORTHERN NIGERIA)

 

 

Kotun daukaka kara da ke shiyyar Sakkwato a arewacin tarayyar Najeriya ta tabbatar da dan takarar Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Dare a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP, a zabe mai zuwa na shekarar 2023 da za a yi a watan Fabrairu mai zuwa.

 

 

Alkalin kotun a halin yanzu ya jingine hukuncin da babbar kotun tarayya da ke Gusau ta yi inda ta hana Dauda Lawal Dare tsayawa takarar Gwamnan.

 

Idan dai za a iya tunawa Injiniya Ibrahim Shehu daya daga cikin yan takarar Gwamnan ne ya kai karar Dauda Lawal bisa abin da ya kira an yi ba dai dai ba a wajen zaben fitar da dan takarar Gwamnan Jihar Zamfara a Jam’iyyar PDP.

About andiya

Check Also

PURPORTED SUSPENSION OF ZAMFARA APC CHAIRMAN, HON. TUKUR UMAR UMAR DANFULANI 

The Zamfara State chapter of the All Progressives Congress APC wishes to draw the attention …

Leave a Reply

Your email address will not be published.