Home / Big News / Batun Nadin Ibrahim Gambari Ban San Maganar Ba – Garba Shehu

Batun Nadin Ibrahim Gambari Ban San Maganar Ba – Garba Shehu

 Imrana Abdullahi
Biyo bayan irin yadda ake ta yayatawa a kafafen Sada zumunta cewa wai shugaba Muhammadu Buhari na tarayyar Nijeriya ya nada Furofesa Ibrahim Gambari a matsayin shugaban ma’aikatan Ofishinsa.
Hakan ta sa aka tuntubi mai magana da yawun shugaban kasar Malam Garba Shehu inda manema labarai suka aika masa sakon tambaya a wayarsa ta hannu domin samun tabbacin labarin.
Sai Malam Garba Shehu ya mayar da sako cewa ” bani da labarin hakan, domin ba a yi mini bayanin komai ba”, inji Garba shehu.
Faruwar hakan dai ya biyo bayan rasuwar shugaban ma aikatan fadar shugaban kasar ne Malam ABBA Kyari.

About andiya

Check Also

Ramadan 2023: Nigerian Church Reaches Out To Over 1000 Underprivileged Muslims/ Almajiri.

  The church of Christ Evangelical and life Intercessory Ministry, Sabon Tasha Kaduna State has …

Leave a Reply

Your email address will not be published.