Home / Big News / Batun Nadin Ibrahim Gambari Ban San Maganar Ba – Garba Shehu

Batun Nadin Ibrahim Gambari Ban San Maganar Ba – Garba Shehu

 Imrana Abdullahi
Biyo bayan irin yadda ake ta yayatawa a kafafen Sada zumunta cewa wai shugaba Muhammadu Buhari na tarayyar Nijeriya ya nada Furofesa Ibrahim Gambari a matsayin shugaban ma’aikatan Ofishinsa.
Hakan ta sa aka tuntubi mai magana da yawun shugaban kasar Malam Garba Shehu inda manema labarai suka aika masa sakon tambaya a wayarsa ta hannu domin samun tabbacin labarin.
Sai Malam Garba Shehu ya mayar da sako cewa ” bani da labarin hakan, domin ba a yi mini bayanin komai ba”, inji Garba shehu.
Faruwar hakan dai ya biyo bayan rasuwar shugaban ma aikatan fadar shugaban kasar ne Malam ABBA Kyari.

About andiya

Check Also

APC Ta Ƙasa Ta Amince Da Gwamna Lawal Domin Takarar Wa’adi Na Biyu A Zamfara

  Jam’iyyar APC ta tantance tare da amincewa da Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, domin …

Leave a Reply

Your email address will not be published.