Home / News / Gwamna Bala Muhammad Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Gwamna Bala Muhammad Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Daga Imrana Abdullahi

Rahotannin da ke fitowa daga Jihar Bauchi na cewa an zabi Gwamna Bala Mohammed a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP.

Kamar dai yadda wata sanarwa daga bakin Gwamna Ahmadu Fintiri na Jihar  Adamawa ne ya bayyana hakan a ranar Asabar din da ta gabata jim kadan bayan wata ganawar sirri da aka yi a gidan gwamnati dake Bauchi.

Kamar dai yadda bayanan ke cewa  da jiga-jigan jam’iyyar 13 sun je Bauchi domin yin taron kwana guda na jami’an da aka zaba a karkashinta.

Fintiri, ya tabbatar da cewa  an zabi Gwamna Siminalayi Fubara na Rivers mataimakin shugaban kungiyar.

Ya ce an zabi Mohammed ne bisa cancantarsa ​​da iya tafiyar da dandalin har zuwa wani matsayi mai girma.

Da yake mayar da martani, Mohammed ya yi alkawarin zai yi tare da takwarorinsa domin ci gaban jam’iyyar da kasa baki daya.

“Bayanai na a matsayina na Shugaban kungiyar Gwamnonin PDP wata alama ce ta girmamawa gare ni da daukacin al’ummar Jihar Bauchi.

“Ina amfani da wannan dama wajen kira ga dukkan abokan aikina da su ba ni goyon baya domin ciyar da dandalin da jam’iyyar gaba,” inji

About andiya

Check Also

Agriculture: Mrs Tinubu empowers 140 North west women farmers as Gov Idris enhances sustained farmers , women capacity for nation building

By Suleiman Adamu, Sokoto At least , 140 Northwest women farmers in Kebbi state benefitted …

Leave a Reply

Your email address will not be published.