Home / Lafiya / Gwamna Radda Ya Kafa Harsashin Cibiyar Wankin Koda (Dialysis)

Gwamna Radda Ya Kafa Harsashin Cibiyar Wankin Koda (Dialysis)

Daga Imrana Abdullahi

Gwamna Dikko Umar Radda ne ya aza harsashin ginin cibiyar kula da lafiya ta duniya a babban asibitin Janar Amadi Rimi da ke yankin karamar hukumar Batagarawa a jihar.

Kakakin Malam Dikko Radda, Ibrahim Kaula Mohammed, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce taron na daga cikin ayyukan da aka tsara domin tunawa da cika kwanaki 100 da ya yi a kan karagar mulki a matsayin gwamnan jihar Katsina.

Kwamishinan lafiya na jihar Dokta Bishir Gambo Saulawa ya bayyanawa manema labarai yadda aikin yake gudana a wani taron tattaunawar da suka yi da shi.

Ya ce Cibiyar wankin Kodar, idan aka kammala ta, za ta kasance daya daga cikin mafi kyau a Arewacin Najeriya. Ya ce za a kafa irin wannan cibiyar kiwon lafiya a garin Funtua don kula da marasa lafiya da ke buƙatar aikin wankin Kodar.

“Tun da dadewa, kuma kafin yanzu, Jahar mu mai kauna tana da injinan wankin Kodar guda hudu a babban asibitin Katsina.

“Ya zuwa lokacin da aka kammala sabbin Cibiyoyin kula da Lafiyar Jiki guda biyu, za mu kasance da na’urorin wankin Kodar guda 16,” in ji shi.

About andiya

Check Also

Group Decries Escalation Of  Insecurity In Birnin Gwari

      By; Our Reporter in Kaduna   The Birnin Gwari Progressive Union(BEPU) has …

Leave a Reply

Your email address will not be published.