Home / Labarai / Shugaban Karamar Hukumar Giwa Ya Taimakawa Mutanen Bakali

Shugaban Karamar Hukumar Giwa Ya Taimakawa Mutanen Bakali

Shugaban karamar hukumar Giwa Alahaji Abubakar Shehu Lawal Giwa ya wallafa wa mutanen garin Bakali da ke gundumar masarautar Fatika cikin karamar hukumar Giwa a Jihar Kaduna.
Kaya
Ga dai irin kayan da aka ba mutane Bakali Tallafi
Shugaban ya kai masu kayan da suka hada da Buhunan Masara 30, Buhunan Shinkafa 20, Katifu 30, man Gyada hakan 25sai Zannuwa 50 da kuma Shadda 50, an dai kai masu wadannan kayan tallafin ne domin su samu saukin matsalar yan Ta’addan da suka kai masu hari a cikin satin da ya gabata.
Kayan Tallafi daga Abubakar shehu Lawal Giwa
on. Abubakar Shehu Lawal Giwa ya kuma yi masu alkawarin ganin hakan bata sake faruwa ba saboda kamar yadda ya bayyana cewa yana ta kokari ba dare ba rana domin ganin ya sadu da wadansu cibiyoyin bayar da agaji ta yadda za a ci gaba da wallafa wa mutanen garin Bakali da ke karamar hukumar.

About andiya

Check Also

Zulum meets Tinubu over South Chad Irrigation Scheme

  .. Says Tinubu approves Gwoza FCE take off     Borno State Governor, Babagana …

Leave a Reply

Your email address will not be published.