Home / Labarai / Yan Bindiga Sun Sace Sarki Kpop Ham Mai Daraja Ta Daya

Yan Bindiga Sun Sace Sarki Kpop Ham Mai Daraja Ta Daya

Mustapha Imrana Abdullahi

Rahotannin da muke samun a halin yanzu daga Jihar Kaduna na cewa yan bindiga sun sace wani Sarki mai daraja ta daya Kpop Ham, Dokta Jonathan Danladi Gyet Maude (JP, OON) wanda sanannen Sarki ne kuma jagoran al’ummar Jaba cikin Jihar Kaduna.

Rahotannin da muke samu na bayanin cewa an sace shi ne a Gonarsa da ke Jihar Nasarawa.

Rundunar tsaro ta Yan Sanda a Jihar Kaduna na cewa su na nan su na tuntubar abokan aikinsu daga Jihar Nasarawa, domin sanin ko yaushe lamarin ya faru.

About andiya

Check Also

Ramadan 2023: Nigerian Church Reaches Out To Over 1000 Underprivileged Muslims/ Almajiri.

  The church of Christ Evangelical and life Intercessory Ministry, Sabon Tasha Kaduna State has …

Leave a Reply

Your email address will not be published.