Home / News / Dantakara Solomon Adamu Ya Samu karbuwa a karamar hukumar Chikun

Dantakara Solomon Adamu Ya Samu karbuwa a karamar hukumar Chikun

…A fito a zabi dan takarar jam’iyyar Lebo- inji dan majalisa Ekene Abubakar Adam
Wadansu yayan jam’iyyar Lebo kenan suna murna da irin karbuwa da kuma karbar da aka yi masu a lokacin zagayen gangamin
Dan takarar majalisar Jihar Kaduna daga karamar hukumar Chikun Mista Solomon kenN take gaisawa da dimbin jama’ar da suka fito domin nuna Soyayyarsu gare shi a lokacin da yake Yakin neman jama’a domin zaben gobe Asabar da za a yi.
Wata daga cikin tawagar da take yi wa dan takara Solomon rakiya kenan
Dan majalisar wakilai ta tarayya karkashin jam’iyyar Lebo Ekene Abubakar Adam’s ya yi kira ga daukacin al’ummar karamar hukumar Chikun da su fito kwansu da kwarkwatarsu su zabi dan takarar majalisar Jihar Kaduna Solomon Adamu domin samun ingantaccen shugabanci a majalisar.
Dan majalisa Ekene Abubakar ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zagayawa domin gangamin fadakar da jama’a muhimmancin zaben jam’iyyar Lebo musamman a karamar hukumar Chikun don ya wakilci jama’a a matakin majalisar jiha.

About andiya

Check Also

Group Decries Escalation Of  Insecurity In Birnin Gwari

      By; Our Reporter in Kaduna   The Birnin Gwari Progressive Union(BEPU) has …

Leave a Reply

Your email address will not be published.