Home / Big News / Shugabannin Kananan Hukumomin Shiyya Ta Daya Sun Tsayar Da Muktar Ramalan Yero Takarar Sanata.

Shugabannin Kananan Hukumomin Shiyya Ta Daya Sun Tsayar Da Muktar Ramalan Yero Takarar Sanata.

 

Daga Imrana Abdullahi
Bayanan da muke samu daga shiyya ta daya cikin Jihar Kaduna da ke arewacin tarayyar Najeriya na cewa daukacin shugabannin Kananan hukumomin da ke shiyyar karkashin jagorancin Malam Jamilu Albani da ke zaman shugaban karamar hukumar Sabon Gari sun tsayar da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Alhaji Dokta Muktar Ramalan Yero takarar Sanatan yankin.

Bayanan da muka samu sun ce hakan ya faru ne a lokacin wani kwarya kwaryan taron da aka yi a garin Zariya hedkwatar shiyyar ta daya.
Sai dai ana saran a nan gaba kadan ne wanda aka tsayar din zai bayyanawa duniya da kansa,  duk da cewa a wajen wannan taron tuni tsohon Gwamnan ya amince da wannan yunkuri na daukacin shugabannin Kananan hukumomin da ke yankin na shiyyar ta daya, karkashin jagorancin Jamilu Albani.

About andiya

Check Also

At the Bullion lecture, RMRDC boss says Dangote Refinery Showcases Power of Domestic Value Addition

…asks Nigerians to pray for Aliko Dangote Public Policy analysts, Government officials and other Stakeholders …

Leave a Reply

Your email address will not be published.